Tugunyar gss tafashe a sabon gari Kano inda mutum hudu sukamutu ๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

Rahotanni daga jihar Kano a arewa maso yammacin Najeriya na cewa bam ya tashi a Aba Road da ke Unguwar Sabon Gari a birnin Kanon.

Shugaban Kasuwar Sabon Gari Nafi'u Nuhu Indabo ya tabbatar wa da BBC lamarin, inda ya ce lamarin ya rutsa da mutane da dama ciki har da yara ฦดan makaranta.

Wakilinmu da Kano Khalifa Dokaji ya je wajen da abin ya faru, wato makarantar Winner Kids Academy da ake zargin a can aka ta da bam din.

"Rufin makarantar ya yaye saboda ฦ™arfin bam ษ—in. Dukkan hanyoyin da suke kusa da wajen sun cika maฦ™il da jama'a waษ—anda ke ciki da damuwa da alhini," in ji Dokaji.

Tuni kwamishinan ฦดan sanda na jihar Kano CP Sama'ila Dikko da shugaban hukumar DSS na jihar sun halarci wajen, sannan motocin asibiti sun je don kwasar waษ—anda harin ya rutsa da su.

Hukumomi ba su kai ga fadin adadin wadanda abin ya rutsa da su ba, amma Khalifa Dokaji ya ce ana iya ganin jini ta ko ina a wajen da kuma wasu sassan jikin mutane.

Jami'an tsaro sun yi ta ฦ™oฦ™arin shawo kan mutane waษ—anda da alama ke fusace, don su bari a yi bincike kan musabbabin faruwar lamarin.

An daษ—e ba a ji labari mai kama da wannan ba wato na kai harin bam a jihar Kanon, dalilin da ya sa hakan zai jefa mutane cikin ruษ—anin wa yake da alhakin hakan.

Ba a Kano kaษ—ai ba, an samu sauฦ™in tashin bam a faษ—in Najeriya a shekarun bayan nan, ba kamar a da ba da hakan ya zama kusan ruwan dare.

Za mu ci gaba da kawo muku ฦ™arin bayani kan labarin, sai ku dinga sabunta wannan shafi.

Post a Comment

Previous Post Next Post