Bazan bari wani ya karya doka a Nigeria bah buhari

  1. Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi kira ga 'yan kasar da su guji mutanen da ke hankoron ganin sun karya doka a kasar.

    Wata sanarwa da kakakin shugaban kasar Malam Garba Shehu ya aike wa manema labarai ta ambato Shugaba Buhari yana mai tabbatar wa 'yan kasar cewa ba zai kyale wani ya karya dokokin kasar ba.

    ''Muna da kasa, muna da albarkatun kasa da kuma mutane. Sai dai ban san dalilin da ya sa wasu ke da niyyar ba da kansu ba wajen lalata ƙasarsu ba," a cewar Buhari yayin buɗe baki da ya yi da gwamnoni da ministoci a Abuja ranar Talata.

    Shugaban ya sake jaddada cewa ƙaddamar da amfani da fasahar na'urar tantance masu kaɗa ƙuri'a "ba za ta bari wani ya yi iƙirarin samun miliyoyin ƙuri'u" yayin babban zaɓe na 2023 mai zuwa.

    Buhari
  2. LABARAI DA DUMI-DUMIBuhari na halartar taron APC kan jadawalin zaɓen fid da gwani

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari na halartar taron Majalisar Zartarwa na jam'iyyar APC mai mulkin ƙasar da ke gudana yanzu haka.

    Ana gudanar da taron ne a otel ɗin Transcop Hilton da ke Abuja karon farko tun bayan da APC ta zaɓi sabbin shugabanninta a watan Maris.

    Ana sa ran 'yan majalisar wanda Buhari na ɗaya daga cikinsu, za su daddale jadawalin zaɓukan fid da gwani na jam'iyyar a matakin shugaban ƙasa da kuma na jihohi.

    Za mu kawo ƙarin bayani da zarar mun samu...

Post a Comment

Previous Post Next Post