Adamu garba, idan na siya form naira 100m za a ce ni barawo ne

Adamu Garba: Idan na sayi fom a kan N100m za a ce ni barawo ne

Danna hoton da ke sama domin kallon bidiyon:

Mutumin da ke neman APC ta tsayar da shi takarar shugabancin Najeriya, Adamu Garba, ya koka kan yadda jam'iyyar ta tsawwala kudin sayen fom din takarar.

A tattaunwarsa da BBC Hausa, ya ce a matsayinsa na mutumin da ke yin aiki a kamfanin mai zaman kansa, ba shi da halin sayen fom din takarar shugaban kasa a kan N100m.

Ya ce ya fito takarar shugaban kasa ce domin kawo sauyi a kasar ganin cewa sauyi ba zai samu sosai ba idan mutum bai hau karagar shugabancin kasar ba.

Sai dai ya ce "miliyaan dari ba karamin kudi ba ne; yanzu haka idan mutanen da nake tare da suka ga na tattara naira miliyan dari na je na biya kudin fom, ai kowa zai ce ni barawo ne."

Post a Comment

Previous Post Next Post