Sheikh Dr. Sani Sharif Umar Bichi shugaban kungiyar Izala mai hesikwata a Jos rashen jahar Kano ya yi jan kunne ga waษanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa akan wannan daliba da ta zagi Annabi SAW.
Malam ya ce “yanzu idan aka ce wadanda suka kasheta su bada sheda kota muryar ta ba za su gane ba sabida ba ta raye, amma da an kaita gurin hukuma a yi bincike a hukumance a yanke mata hukunci daidai da abinda ta yi”.
Malam ya kara da cewa “duk da idan aka kai gurin hukuma ba sa yin abin da ya dace, ko da wani abu na laifi ya faru, babu wani wanda yake da hakkin zartar wa wani haddi ko hukunci akan tuhumar da ake masa, har sai an gabatar da shi gaban alkali, shi ne wanda zai iya tabbatar masa da wannan laifin ko ya wanke shi idan koto ce takamat ta hukunta cewar Malam .