innalillh Kai duniya wani magudanci ya kashe matarsa sannan ya rarake mata idanu

Ana tuhumar wani magidanci mai shekaru 32 a duniya bisa halaka matarsa mai suna Mercy Samuel a Jos, babban birnin jihar Filato da ke a yankin arewacin Najeriya.

Bbc hausa ta samo cewa hukumomi a jihar Filato sun tabbatar da aukuwar lamarin, inda kwamishiniyar kula da harkokin mata ta jihar Filato, Rebecca Sambo ta shaida wa BBC Pidgin cewa lamarin ya auku ne a daren ranar 17 ga watan Afrilu.

Ta bayyana cewa magidancin ya farke wa matar sa ciki da misalin ฦ™arfe biyu na dare, sannan  ya cire mata ‘yan hanjinta.

Mercy mai shekaru 25 a duniya, ta mutu bayan an garzaya da ita zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Bingham a Jos, domin  a yi mata tiyata.

Hukumar ‘yan sandan Filato ta bayyana cewa tana kan gudanar da bincike dangane da lamarin.

Magidancin da matar tasa Mercy sun kasance tare a ฦ™arฦ™ashin igiyar aure har na tsawon shekaru 9, sannan sun haifi yara guda biyu a tare.

Dan uwanta ya bayyana cewa cikin tsakar dare makwabta suka ji tana kurma ihu, ko da aka fito domin kawo mata ษ—auki sai aka tarar da ‘yan hanjin cikinta a hannunta.

Yanzu haka ‘yan sanda na kan farautar magidanci ruwa ajallo wanda tuni tsere.   Magidancin yana dukan matar sa duk lokacin da su ka samu ฦ™aramin saษ“ani. Na samu na ษ—auki abinda ya faru yau. Musulmi ne, ina tunanin sun samu saษ“ani ne akan abincin Sahur.

Magidancin bai damu da cewa tana ษ—auke da cikin ษ—an sa na biyu ba, ya cigaba da dukan ta. Ta yi ta ihu sannan daga bisani ta samu ta gudu zuwa gidan iyayen ta. Gbolagade ya tsere daga gidan sa bayan ‘yan sanda sun bada sanarwar neman sa ruwa a jallo.

Post a Comment

Previous Post Next Post